Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta amince da sake buɗe iyakar ƙasa ta Tsamiya da ke jihar Kebbi domin ci gaba da kasuwancin ƙetare iyaka, tare da sanya tsauraran matakan tsaro da bin ƙa’idoji.
Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS), CG Adewale Adeniyi, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a jihar Kebbi, ciki har da ’yan kasuwa, masu safarar kaya da kuma ’yan kasuwar albasa.
Adeniyi ya ce matakin sake buɗe iyakar ya biyo bayan umarnin Gwamnatin Tarayya, inda ya jaddada cewa za a gudanar da kasuwancin ne cikin kulawa ta musamman domin tabbatar da tsaro da bin dokokin kwastam.
Gwamnatin Nijeriya ta amince da sake buɗe bodar Tsamiya da ke jihar Kebbi domin haɓɓaka kasuwanci
-


