DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Sokoto ta nesanta kanta da kyautar mota da shago da aka bai wa Rahama Saidu

-

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana cewa ba ta da wata alaƙa da batun bai wa ƴar TikTok Rahama Saidu mota da shago, wanda wani mai suna Sanin Jaman ya yi, a wani faifan bidiyo ya karade kafafen sada zumunta.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Ofishin Mai Magana da yawun Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, ya fitar a ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce, Sanin Jaman ya bayyana cewa kyautar da ya bai wa Rahama Saidu a kashin kansa ne, domin nuna godiya da yabon da take yi wa gwamnatin Ahmad Aliyu a jihar Sokoto.

Sai dai gwamnatin jihar ta jaddada cewa ba ta da hannu ko alaƙa da wannan kyauta, tare da nesanta Gwamna Ahmad Aliyu da gwamnatin jihar Sokoto daga lamarin baki ɗaya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara