Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya bai wa kwangiloli kwanaki uku su kammala share shara a garuruwan Abuja ko kuma fuskantar dakatar da kwangilarsu.
Wike ya bayar da wannan gargadi ne bayan ziyarar duba ayyukan hanyoyi a Karu, Bwari, Kubwa da hanyar Apo–Karshi a Abuja ranar Juma’a.
Ministan ya nuna damuwa kan tarin shara da ke ƙaruwa a gefen hanyar Orozo–Apo–Karshi yayin ziyarar.


