Masana harkokin lafiya sun bukaci Gwamnatin Tarayya da ta ba da fifiko wajen samarwa da wadatar da maganin harbin maciji (antivenom) a asibitoci fadin Nijeriya, yayin da rahotanni ke nuna cewa kasar na samun kusan harbin maciji 43,000 a duk shekara.
Manyan kwararrun lafiyar sun bayyana cewa karancin samun wannan muhimmin magani na ci gaba da haddasa mutuwar mutane da dama da maciji ke harba a kasar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Sun kuma nuna cewa baya ga karancin maganin, wadanda harbin maciji ya shafa na kashe tsakanin N180,000 zuwa N250,000 a kan kashi daya na maganin, adadin da ya kai kusan albashin watanni hudu ga ma’aikacin da ke karbar mafi karancin albashi na N70,000 a Nijeriya.
A cikin wata sanarwar bayan wani taro kan kula da harbin maciji da hanyoyin bincike, wanda aka wata kungiya ta gudanar a Jami’ar Gombe, kungiyar ta bayyana lamarin a matsayin matsalar da aka yi watsi da ita, duk da irin barnar da take haifarwa a fadin kasar.


