DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NLC ta yi barazanar zanga-zanga kan “ruɗani” kan dokar zaɓe da majalisa ke gyara

-

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi gargaɗin yiwuwar zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da kuma kaurace wa zaɓe, sakamakon abin da ta kira ruɗani da saɓanin matsaya daga Majalisar Dattawa kan gyaran Dokar Zaɓe, musamman game da aika sakamakon zaɓe ta na’ura.

Kungiyar ta zargi Majalisar Dattawa da watsi da buƙatar jama’a ga tsarin zaɓe a Nijeriya, saboda kasa fayyace ko aika sakamakon zaɓe ta na’ura tilas ne ko a’a.

Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, inda ya ce kungiyar na nuna damuwa mai tsanani kan “ruɗani da bayanai masu karo da juna” da ke fitowa daga Majalisar Dattawa dangane da gyaran Dokar Zaɓe ta 2022, musamman a kan batun e-transmission.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara