Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya gargadi gwamnonin da sauran ’yan siyasa da ke goyon bayan Gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara, cewa goyon bayan “cin amana” zai koma musu.
Wike ya bayyana haka ne yayinda yake jawabi wajen taro ranar Asabar a birnin Fatakwal na jihar Rivers, ya ce duk wanda ke mara wa mai cin amana baya, shi ma za a ci amanarsa a nan gaba.
Rikicin Wike da Fubara ya samo asali ne daga takaddamar a siyasar Rivers, duk da ƙoƙarin sulhu da aka yi, har zuwa wannan lokaci rikicin na ci gaba da shafar harkokin siyasa a jihar.



