DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka na iya taka rawar gani fiye da na ‘yar kallo a zaben 2027 – Yakubu Dogara

-

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilan Nijeriya, Yakubu Dogara, ya yi gargadin cewa Amurka na iya taka rawa mai zurfi, ba wai ta zura ido ba kawai, a zaben gama-gari na Nijeriya na shekarar 2027.

Dogara ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi a gidan talabijin na Channels, inda ya ce sha’awar Amurka ta samo asali ne daga muhimmancin Nijeriya ga zaman lafiyar Afirka da kuma muradun Amurka na kasa da kasa.

Google search engine

Ya ce tsarin hulda tsakanin kasashe na duniya ya raunana, inda kasashe ke kara tsananta kare muradunsu.

Dogara ya ce Amurka ba za ta so Nijeriya ta durkushe ba, domin hakan na iya haifar da mummunan tasiri ga Afirka baki daya, don haka zai zama cikin muradunsu su sa ido sosai kan zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara