Bayanai daga shafin jaridar New York Times sun nuna cewa gwamnatin Amurka na shirin aikewa da karin dakarun sojinta zuwa Nijeriya.
Hakan dai kari ne ga jami’an da Amurkan ta fara tura wa zuwa kasar a makon da ya gabata, kamar yadda babban kwamandan sojin Amurka da ke Afirka Janar Dagvin R Anderson ya tabbatar.
Bayanan da suka fito sun nuna cewa dukkanin dakarun za su taimaka ne wajen bai wa sojojin Nijeriya horo, ba tare da sa hannu a ko wane irin aikin sanar da tsaro ba.



