Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi hasashen saukar damina da wuri a shekarar 2025, musamman a jihohi irin Kano, Neja, River da wasu 12.
Ministan harkokin sufurin jiragen saman kasar Festus Keyamo ne ya bayyana hakan a Abuja, inda ya gargadi manoma da su guji fara shuka da wuri don gujewa fuskantar kalubale a kan kayan amfanin gona.
Ministan ya kara da cewa duk da kasancewar an fara samun saukar ruwan sama a wasu yankunan Nijeriya, akwai yiwuwar samun sauran lokaci kafin ainahin damina ta fadi, kamar yadda Dailytrust ta ruwaito.



