DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mafi yawan ‘yan majalisar dokokin Nijeriya za su fadi zabe in da gaskiya a ciki – Sowore

-

Dan gwagwarmaya a Nijeriya Omoyole Sowore ya ce kaso 90 na ‘yan majalisar dokokin kasar ba za su koma kujerunsu ba in har za a gudanar da zabuka cikin gaskiya.

 

Google search engine

Sowore ya bayyana haka ne a matsayin marokan cece-kucen da ya barke game da batun gyaran dokar zabe, musamman sashen da ke magana kan aikewa da sakamako ta hanyar amfani da yanar gizo.

 

Da yake tattaunawa da gidan talabijin na Channels cikin shirin safiya, Sowore ya zargi ‘yan majalisun da kin bullo da dokokin da za su tabbatar da sahihancin zabuka a kasar, domin suna tsoron rasa kujerunsu.

 

A cewar sa, hujjar da aka gabatar ta cewa rashin yanayin sadarwa mai kyau zai tilasta yin amfani da takardu, tana nuna gazawa wajen kokarin tabbatar da adalci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara