‘Yan vigilante sun kwankwashi kan wani matashi da kusa bayan sun zarge shi da satar kaza a Zaria jihar Kaduna.
Mahaifin matashin, Malam Salisu Nuhu wanda aka fi sani da Babandede, ya tabbatar da lamarin tare da zargin jami’an vigilante biyu da yin aika-aikar.
A cewar sa, shi ne ya aiki dan nasa ya siyar da kaza a kasuwa, kafin jami’an su zarge shi da sata kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Tuni dai DPO na ‘yansandan yankin na Zaria Nura Abubakar ya ce an cafke mutum guda da ake zargi cikin jami’an, tare da shan alwashin gudanar da cikakken bincike.



