DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yansanda sun cafke ‘Dan da ake zargi wajen yin garkuwa da mahaifinsa a Adamawa

-

Jami’an ‘yansanda a jihar Adamawa sun cafke wani matashi da ake zargi da hada baki da ɓata-gari wajen yin garkuwa da mahaifinsa.

Mai magana da yawun rundunar SP Suleiman Nguroje ya tabbatar da kamen wadanda ake zargi da aikata laifin, bayan gudanar da binciken sirri da kuma hadin gwiwa da jami’an sa kai, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Google search engine

A cewar sa, rundunar ta dauki mataki ne bayan korafin da aka shigar gabanta na batan mutumin mai suna Alhaji Ahmadu a garin Malabu da ke karamar hukumar Fufore a jihar Adamawa.

A cewar sa, duka matasa ukun da aka kama sun amsa hannu a sace shi, ciki har da dansa na cikinsa, kuma rundunar tana ci gaba da bincike don ceto wanda aka yi garkuwa da shi cikin koshin lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara