Mai shari’a Obiora Egwuatu ya janye kansa daga shari’ar da hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arziki zagon kasa ta Nijeriya ta shigar da tsohon ministan shari’ar Nijeriya Abubakar Malami SAN.
Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito Alkalin na cewa ya janye daga shari’ar ne saboda dalilai na kashin kai da kuma barin gaskiya ta yi halinta.
Jerin shari’a guda biyu ce dai EFCC ta shigar da Abubakar Malami a gaban kotu kan mabambantan zarge-zarge.



