Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa ta kama wasu matasa 3 da take zargi da fyace majina da N500 a Maiduguri jihar Borno.
Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook, EFCC ta bayyana sunayen matasan da Adam Muhammad, Muhammad Muhammad da kuma Bashir Musa.
Hukumar ta cafke matasan ne bayan da wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta ya nuna matasan na share majina da takardar kudi ta Naira 500.
Haka kuma hukumar ta ce za ta gurfanar da su a gaban kotu da zarar ta kammala bincike.



