Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya tafi birnin Addis Ababa na Ethiopia domin wakiltar shugaba Tinubu a taron kungiyar tarayyar Afirka na 2026.
Baya ga taron kungiyar, Kashim Shettima zai halarci wasu tarukan da kuma ganawa da jagororin Afirka a bangarori daban daban, da nufin karfafa alakar Nijeriya da wasu kasashen a Afirka.
Ya samu rakiyar wasu ministoci da kuma manyan jami’an gwamnati, kuma ana sa ran zai koma gida Nijeriya bayan kammala duka tarukan, kamar yadda fadar shugaban kasa ta sanar.



