DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ADC ta soki yunƙurin kama El-Rufai tare da zargin gwamnati da tsoratar da ‘yan adawa

-

Jam’iyyar ADC ta yi Allah-wadai da abin da ta kira yunƙurin kama tsohon gwamnan Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, a filin jirgin sama ba tare da sammaci ba, tana mai cewa hakan na tayar da tambayoyi kan bin doka da nuna bangaranci.

A sanarwar da Sakataren Yada Labarai na Kasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta ce bai kamata doka ta zama makamin yaki da ‘yan adawa ba, duk da cewa babu wanda ya fi karfinta.

Google search engine

ADC ta kuma zargi gwamnatin APC ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu da nuna bambanci a yaki da cin hanci, tana mai cewa ana tsananta bincike kan masu sukar gwamnati yayin da wasu ke samun karɓuwa a jam’iyya mai mulki.

Jam’iyyar ta bukaci hukumomin tsaro su kiyaye kwarewa da kundin tsarin mulki, tare da jaddada cewa ya kamata siyasa ta gudana ta hanyar kuri’a da hujja, ba ta hanyar tsoratarwa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara