DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar NDLEA ta kama buhunnan tabar wiwi 64 a Kano

-

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) reshen Kano ta kama buhuna 64 na tabar wiwi da aka boye a cikin wata tirelar siminti a kan titin Kano–Zariya. Kakakin rundunar, ASN Sadiq Maigatari, ya ce an kama kayan ne ranar 2 ga Fabrairu, 2026, bayan samun bayanan sirri da sa ido na musamman.

Ya ce tirelar dauke da simintin Dangote ta taso daga Obajana a Jihar Kogi zuwa Mubi a Adamawa, kafin jami’ai su tsaida ta a kan titin Zariya–Kano. An kama direban motar, wanda ke hannun hukuma domin ci gaba da bincike.

Google search engine

Kwamandan NDLEA na Kano, D.Y. Lawal, ya ce an boye miyagun kwayoyin cikin kaya na halal, kuma ana zargin an shirya rarraba su ne a Kano gabanin watan Ramadan. Ya jaddada cewa ba za su bari masu fatauci su lalata al’umma ba.

Hukumar ta ce za ta kara tsaurara sintiri da bincike a fadin jihar, tare da bin diddigin wadanda ke da hannu a lamarin domin gurfanar da su a gaban kuliya. Ta kuma bukaci jama’a su rika bayar da bayanai kan duk wata alama ta fataucin miyagun kwayoyi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

NNPP ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya ta wanke Kwankwaso daga zargin tallafa wa ta’addanci

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya da Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA) su fito su wanke jagoranta na...

Kotu a Kano ta daure jarumar Kannywood Samha Inuwa watanni 6 a gidan gyaran hali

Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, Mai shari’a S.M. Shuaibu, ya yanke wa jarumar Kannywood, Saadatu Mohammed Inuwa wadda aka fi sani da Samha,...

Mafi Shahara