DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jonathan da Akume sun saba wa juna kan ka’idar shekarun shugabanci

-

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bukaci Afirka ta bai wa matasa damar shugabanci, yana mai cewa shekaru 25 zuwa 50 sun fi dacewa da juriya da kuzarin zamani, inda ya ambaci Murtala Muhammed da Yakubu Gowon a matsayin shugabannin matasa masu tasiri.

Sai dai Sanata George Akume, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, ya jaddada cewa shugabanci ba ya ta’allaka da shekaru, sai da hangen nesa da kwarewa, inda ya ce tasirin shugaba na fitowa ne daga tunani da iya aiki.

Google search engine

A taron da aka yi don tunawa da cika shekaru 50 da kisan Janar Murtala Muhammed, tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya danganta koma bayan tattalin arzikin Nijeriya da sauya manufofi ba tare da dorewa ba, musamman shigo da shinkafa tun 1979.

Obasanjo ya yi kira ga Afirka da ta mayar da hankali kan gyare-gyare masu dorewa da karfafa samarwa domin samun ci gaba mai ma’ana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

NNPP ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya ta wanke Kwankwaso daga zargin tallafa wa ta’addanci

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya da Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA) su fito su wanke jagoranta na...

Kotu a Kano ta daure jarumar Kannywood Samha Inuwa watanni 6 a gidan gyaran hali

Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, Mai shari’a S.M. Shuaibu, ya yanke wa jarumar Kannywood, Saadatu Mohammed Inuwa wadda aka fi sani da Samha,...

Mafi Shahara