Majalisar Dokokin Nijeriya ta sanar da cewa za ta yi zama na gaggawa a ranar Talata, 17 ga Fabrairu, 2026, domin duba yiwuwar sauya ranar da aka sanya zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Jaridar Punch ta rawaito cewa majalisar na shirin matsar da ranar zaɓen shugaban ƙasar daga 20 ga Fabrairu zuwa 13 ga Fabrairu, 2027, bayan samun korafe-korafe daga masu ruwa da tsaki.
A wata sanarwa da magatakardan majalisar, Kamoru Ogunlana ya fitar, an umarci sanatoci da ‘yan majalisar wakilai su koma a ranar Talata, domin daukar matakai da ke da muhimmanci.



