Mai ba Gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, Dahiru Abdulsalam, ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan taron tsaro da mataimakin Gwamnan jihar, Idi Barde Gubana, ya jagoranta.
A cewarsa, kwamitin tsaron jihar ya ga dacewar sassauta dokar ne domin bai wa Musulmi damar gudanar da ayyukan addini cikin sauƙi a lokacin azumi.
Ya bayyana cewa an kira taron tsaron ne domin tantance yanayin tsaro a faɗin jihar, tare da tabbatar da cewa al’umma sun gudanar da kwanaki 30 na azumi cikin lumana, tare da kare rayuka da dukiyoyinsu yadda ya kamata.



