An dauki matakin dakatar da shirin tsige gwamnan ne a yayin zaman majalisar da ke gudana a birnin Fatakwal na jihar ta Rivers.
Tun da fari, majalisar ta soma shirin tsige Gwamna Fubara da mataimakiyarsa bisa zargin aikata manyan laifuffuka da suka haɗa da rushe ginin majalisar dokoki da kashe kuɗaɗe ba tare da amincewar majalisa ba, da sauran zarge-zarge.
Kakakin majalisar dokokin jihar, Martin Amaewhule, ne ya jagoranci zaman da aka dakatar da shirin.



