DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya za ta kafa kwalejin koyon likitanci ta sojoji don magance karancin likitoci

-

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da shirin kafa kwalejin koyon likitanci ta soji “Armed Forces College of Medicine and Health Sciences” a matsayin wani mataki na dakile karancin likitoci da cike giɓin likitoci 340,000 a Nijeriya.

Shirin ya biyo bayan taron ministoci da suka haɗa da ministan ilimi Dr. Maruf Tunji Alausa, karamar minstar ilimi Suwaiba Ahmed, da ministan tsaro, Christopher Musa, tare da sauran masu ruwa da tsaki a fannin ilimi, lafiya da tsaro.

Google search engine

Kwalejin za ta zama wata hanya ta ƙarfafa ayyukan kiwon lafiya na sojoji, horar da likitoci da masu jinya, masu kwarewa wajen kula da masu raunin a wajen yaki, da kuma samar da karin likitoci a fadin ƙasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotu ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami zuwa 27 ga Fabrairu

Kotun tarayya da ke Abuja ta ɗage shari’ar tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami, tare da ɗansa Abdulaziz, zuwa 27 ga Fabrairu, 2026. Alƙaliyar kotun, Joyce Abdulmalik,...

Kotu a Marocco ta yanke wa magoya bayan Senegal da suka ta da tarzoma a gasar AFCON 2025 hukunci

Wata kotu a ƙasar Morocco ta yanke wa magoya bayan Senegal 18,hukunci bisa laifin ta da tarzoma a wasan karshe na cin kofin Nahiyar Afrika...

Mafi Shahara