DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ICPC na bin diddigin ayyukan mazaɓu na Naira biliyan 13.5 a Katsina

-

Hukumar ICPC mai yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta kaddamar da Mataki na 8 na shirin bibiyar ayyukan mazabu da na sashen zartarwa a Jihar Katsina, inda ake sa ido kan jimillar ayyuka 39 da kudinsu ya kai naira biliyan 13.5 a yankunan sanatoci da mazabun tarayya na jihar.

A cewar hukumar, tawagar bibiyar ayyukan ta hada da manyan jami’ai daga hedikwata da ofishin Katsina.

Google search engine

Hukumar ta ce ana gudanar da aikin ne tare da hadin gwiwar Nigerian Institute of Quantity Surveyors da kafafen yada labarai domin tabbatar da inganci, amfani da kudi yadda ya dace, da bin ka’idojin ayyuka.

Tuni an duba ayyukan cibiyoyin lafiya a birnin Katsina, hanyoyi a Funtua da Kankia, da ayyukan samar da ruwa a Kurfi, Dutsin-Ma, Mashi da Dutsi. Haka kuma an bibiyi ayyukan makarantu a Kafur, Sandamu, Daura da Mai’Adua, tare da fitilun kan tituna na hasken rana da shirye-shiryen tallafa wa al’umma.

Hukumar ta ce shirin na gudana karkashin kulawar kwamishinan da ke kula da jihar Katsina, Mr Ludam S. Samuel, a wani yunkuri na kara habaka gaskiya da rikon amana a ayyukan gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya yi kira da a zauna lafiya gabanin zaɓen Abuja, Kano da Rivers

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a, jami’an tsaro da jami’an Hukumar zaɓe Mai zaman kanta (INEC) da su gudanar...

Gwamnatin Nijeriya za ta kafa kwalejin koyon likitanci ta sojoji don magance karancin likitoci

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da shirin kafa kwalejin koyon likitanci ta soji "Armed Forces College of Medicine and Health Sciences" a matsayin wani mataki na...

Mafi Shahara