DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Chadi na tattauna yiwuwar dawowar dakarun Faransa kasarta

-

Rahotanni daga kafafen yada labarai na kasa da kasa sun nuna cewa tattaunawa ta yi nisa tsakanin ƙasar Chadi da Faransa kan yiwuwar sake dawowar dakarun Faransa a kasar, shekara guda bayan ficewarsu a hukumance.

Sai dai har zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga mahukuntan N’Djamena ko na Paris da ke tabbatar da hakan.

Google search engine

Sojojin Faransa sun kammala ficewa daga Chadi a karshen watan Janairun 2025, bayan da gwamnatin kasar ta bukaci hakan a watan Nuwamban 2024, tare da kalubalantar yarjejeniyar tsaro da ta hada kasashen biyu tun shekarar 1966.

Ficewar Faransa daga Chadi ya zo ne a cikin guguwar korar dakarunta daga yankin Sahel, inda lamarin ya fara daga Mali, ya wuce Burkina Faso, sannan ya isa Jamhuriyar Nijar kafin Chadi ta bi sahu.

Majiyoyi sun ce tattaunawar ta kara karfi ne bayan wani babban taron koli kan huldar kasashen waje da aka gudanar a karshen watan Janairun 2026, tsakanin Shugaban Chadi, Mahamat Idriss Deby, da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara