Rahotanni daga kafafen yada labarai na kasa da kasa sun nuna cewa tattaunawa ta yi nisa tsakanin ƙasar Chadi da Faransa kan yiwuwar sake dawowar dakarun Faransa a kasar, shekara guda bayan ficewarsu a hukumance.
Sai dai har zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga mahukuntan N’Djamena ko na Paris da ke tabbatar da hakan.
Sojojin Faransa sun kammala ficewa daga Chadi a karshen watan Janairun 2025, bayan da gwamnatin kasar ta bukaci hakan a watan Nuwamban 2024, tare da kalubalantar yarjejeniyar tsaro da ta hada kasashen biyu tun shekarar 1966.
Ficewar Faransa daga Chadi ya zo ne a cikin guguwar korar dakarunta daga yankin Sahel, inda lamarin ya fara daga Mali, ya wuce Burkina Faso, sannan ya isa Jamhuriyar Nijar kafin Chadi ta bi sahu.
Majiyoyi sun ce tattaunawar ta kara karfi ne bayan wani babban taron koli kan huldar kasashen waje da aka gudanar a karshen watan Janairun 2026, tsakanin Shugaban Chadi, Mahamat Idriss Deby, da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron.



