DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gambiya ta nuna damuwa kan ’yan kasarta da ke shiga yake-yake a ketare

-

Gwamnatin Gambiya ta bayyana matukar damuwa kan rahotannin da ke nuna cewa wasu ’yan kasarta na tafiya kasashen waje domin shiga yake-yake a turai.

A wata sanarwa da ma’aikatar yada labarai ta kasar ta fitar, ta ce an samu bayanan cewa wasu ’yan Gambiya sun rasa rayukansu bayan shiga yakin kasashen ketare. Sai dai sanarwar ba ta ambaci yakin Ukraine kai tsaye ba.

Google search engine

Binciken da kamfanin dillancin labarai na Agence France-Presse (AFP) ya gudanar ya nuna cewa Rasha na daukar maza ’yan Afirka da alkawarin samar musu da ayyukan farar hula masu tsoka, amma daga bisani a tura su fagen daga a Ukraine.

Sauran kasashen Afirka da suka hada da Najeriya, Kenya da Afirka ta Kudu su ma sun nuna damuwa kan yadda ake daukar ’yan kasashensu domin shiga yakin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara