Gwamnatin Gambiya ta bayyana matukar damuwa kan rahotannin da ke nuna cewa wasu ’yan kasarta na tafiya kasashen waje domin shiga yake-yake a turai.
A wata sanarwa da ma’aikatar yada labarai ta kasar ta fitar, ta ce an samu bayanan cewa wasu ’yan Gambiya sun rasa rayukansu bayan shiga yakin kasashen ketare. Sai dai sanarwar ba ta ambaci yakin Ukraine kai tsaye ba.
Binciken da kamfanin dillancin labarai na Agence France-Presse (AFP) ya gudanar ya nuna cewa Rasha na daukar maza ’yan Afirka da alkawarin samar musu da ayyukan farar hula masu tsoka, amma daga bisani a tura su fagen daga a Ukraine.
Sauran kasashen Afirka da suka hada da Najeriya, Kenya da Afirka ta Kudu su ma sun nuna damuwa kan yadda ake daukar ’yan kasashensu domin shiga yakin.



