DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan 99 domin rigakafin cutar mahaukacin kare

-

Gwamnatin jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan 99 domin fara shirin rigakafin cutar mahaukacin kare (rabies), inda ake sa ran yi wa akalla karnuka 10,000 allurar rigakafi a mataki na farko.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktar Wayar da Kai ta Ma’aikatar Raya Dabbobi ta jihar, Halima Gadanya, ta fitar a ranar Asabar.

Google search engine

Sanarwar ta ce gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ne ya bayar da amincewar a matsayin wani bangare na kokarin gwamnatinsa na kare lafiyar al’umma daga cututtukan da ake iya kauce musu amma masu hadari.

Shirin zai kasance karkashin jagorancin Ma’aikatar Raya Dabbobi ta jihar, inda kwamishinan ma’aikatar, Aliyu Isah Aliyu, zai kula da aiwatar da shi kamar yadda jaridar Punch ta ambato.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya koka kan ƙarancin masu fitowa zabe a Abuja

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda ake gudanar da zaɓen kananan hukumomi cikin lumana a fadin Abuja, duk da...

Babu jam’iyyun NNPP, PDP, da ADC a takardun zaɓen cike gurbi na Kano

Rahotanni daga Arise News sun nuna cewa manyan jam’iyyun adawa guda uku, NNPP, PDP, da ADC ba su bayyana a takardun zaɓe na zaben cike...

Mafi Shahara