Asusun ba da lamuni na Duniya ya cimma yarjejeniya da hukumomin ƙasar Nijar, a wani shiri na bayar da wasu tallafi ga kasar, inda Nijar za ta karɓi kusan dala miliyan 91 wato sama da biliyan 50 na FCFA.
A cewar IMF, ana sa ran tattalin arzikin Nijar zai haɓaka da kashi 6.7% zuwa shekarar 2026, duk da ƙalubalen tsaro da sauyin yanayi da kasar ke fuskanta.



