Ministan sufurin jiragen saman Nijeriya, Festus Keyamo, ya soki jam’iyyun adawa kan martaninsu game da zaɓen ƙananan hukumomin Abuja, yana cewa yawanci sukan amince da sahihancin zaɓe ne kawai idan aka ayyana su a matsayin masu nasara.
Keyamo ya bayyana cewa irin waɗannan kalamai na iya raunana amincewar jama’a da tsarin dimokuraɗiyya, inda ya bukaci ’yan siyasa su riƙa karɓar sakamakon zaɓe cikin girmamawa, ko sun yi nasara ko sun sha kaye.



