DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NNPP ta zargi gwamnatin Kano da farautar masu yi mata adawa

-

Jam’iyyar NNPP a jihar Kano ta zargi gwamnatin jihar da kai wa mambobinta hari abin da jam’iyyar ta ce ba su dace da ka’idojin dimokuradiyya ba.

A wata sanarwa da sakataren yada labaran NNPP na Kano, Injiniya Ibrahim Karaye, ya fitar, jam’iyyar ta ce gwamnati ta fara janye kujerun aikin Hajji da aka riga aka ware wa wasu daga cikin mambobinta, ciki har da tsofaffin kwamishinoni, masu ba da shawara da wasu shugabannin jam’iyyar.

Google search engine

NNPP ta ce wadannan mutane ’yan Kano ne, kuma suna da ’yancin cin irin wadannan abubuwa da gwamnati ke samarwa.

Haka kuma, jam’iyyar ta zargi gwamnati da tsangwama da tsoratar mambobinta domin mayar da motocin aiki da aka ba su a lokacin da suke kan mukamai, tana mai cewa motocin na daga cikin hakkokinsu da suka yi hidima.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’an tsaron Chadi hudu sun kwanta dama a wata fafatawa da wasu mahara a arewacin kasar

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar 17, ga watan Febarairun da muke ciki a lokacin da wata motar jigilar wani kamfani ke cikin tafiya...

Masu zanga zanga a Sénégal na neman adalci ga dalibin Jami’ar Cheikh Anta Diop ta birnin Dakar da aka halaka

Masu zanga zangar da suka hada da magoya bayan jam'iyya mai mulki ta Pastef sun amsa kiran wata hadaka ce ta dalibai da 'yan fafutikar...

Mafi Shahara