Shugaba Tinubu ya taya waɗanda suka samu nasara a zaɓen ƙananan hukumomin Abuja da kuma zaɓen cike gurbi da aka gudanar a jihohin Kano da Rivers.
Shugaban ƙasar ya bayyana cewa sakamakon zaɓukan na nuna ci gaban dimokiraɗiyya da yanayin siyasa a ƙasar, inda ya buƙaci dukkan ɓangarori su mutunta zaɓen da masu kaɗa kuri’a suka yi.
Haka kuma, Tinubu ya yaba da jagorancin ministan Abuja Nyesom Wike, yana mai cewa rawar da ya taka ta taimaka wajen tabbatar da tsari, zaman lafiya da nasarar gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali.



