DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka za ta koro karin ‘yan Nijeriya 19 gida kan aikata munanan laifuka

-

Gwamnatin Amurka ta kara sanya sunayen ‘yan Nijeriya 19 cikin kundin masu munanan laifuka, yayin da ta ke shirin kora su gida.

Wasu bayanai daga shafin yanar gizo na ma’aikatar tsaron cikin gidan Amurka sun nuna cewa mutanen da aka kara, sun sa adadin wadanda za a kora gida ya kai 113.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito cewa laifukan da ‘yan Nijeriyar suka aikata sun hadar da safarar miyagun kwayoyi, cin zarafi, damfara da wasu miyagun laifuka.

Ma’aikatar tsaron ta bayyana cewa da zarar ta kammala bin matakan da suka dace, za ta kora mutanen gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar tace fina-finai ta Kano ta soke lasisin wani gidan gala bisa dalilai na tsaro

Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta soke lasisin gudanar da ayyukan wani gidan gala mai suna Sunsiro Entertainment, wanda ke kan titin Yahaya Gusau,...

Dimukuradiyyar Nijeriya na cikin barazana a mulkin Tinubu – Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya Atiku Abubakar ya nuna damuwa kan karancin fitowar masu kada kuri'a a zaben da aka gudanar ranar Asabar a Abuja. Cikin wani...

Mafi Shahara