Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa zargin da ke yawo a wasu rahotannin kafafen yada labarai na duniya na cewa an biya kaso mai tsoka na kudin fansa domin ceto daliban da aka sace daga makarantar St. Mary’s a Jihar Niger, ba gaskiya ba ne, sannan rahotannin ba su da tushe.
Ministan Yada Labaran kasar Mohammed Idris, ya ce babu wasu kudin fansa da aka biya, kuma babu wani kwamandan ‘yan ta’adda da aka saki. Ministan ya jaddada cewa hukumomin tsaro sun musanta irin wadannan ikirari tun da farko.
Ya ambaci Ofishin Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro, Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), da shugabannin Majalisar Dokoki ta Kasa, yana mai cewa duk sun fito karara sun musanta batun biyan kudin fansa.
Gwamnatin ta ce nasarar ceto daliban ba tare da asarar rai ba, sakamakon aikin leken asiri da tsare-tsaren soji ne. Ta kuma gargadi kafafen yada labarai da su rika tantance sahihancin bayanai kafin wallafawa, tana mai cewa rahotannin da ba su da tabbaci na iya karfafa gwiwar masu aikata laifi ko rage kwarin gwiwar jami’an tsaro.



