Majalisar Wakilan Nijeriya, ta ɗage komawar zaman majalisa daga Talata, 24 ga Fabrairu 2026, zuwa Alhamis, 5 ga Maris 2026.
Sakataren Majalisar, Kamoru Ogunlana, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a daren Litinin, inda ya ce an ɗauki matakin ne domin bai wa kwamitoci damar kammala zaman kare kasafin kuɗi da suke yi.
A cewarsa, an ɗage komawar zaman ne saboda buƙatar kwamitocin majalisar su kammala tattaunawa da ma’aikatun gwamnati, hukumomi da cibiyoyi, kan kasafin kuɗin shekarar 2026.



