A wani rahoto da EF SET na shekarar 2025 ta fitar kasar Afirka ta Kudu ce ta ke kan gaba a jerin ƙasashen Afirka wajen ƙwarewar harshen Turanci.
Rahoton ya nuna cewa ƙididdigar ta dogara ne kan sakamakon kusan miliyan 2.2 daga ƙasashe da yankuna 123 na duniya da suka shiga tsarin.
A kasashen Afrika Zimbabwe ce ta zo ta biyu a kasashen da ke da kwarewa wajen harshen Turanci,Kenya ta zo ta uku,Zambia ta hudu yayinda Nijeriya ta zamo ta biyar a cikin jerin da EF SET ta fitar.



