Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ba shi da dan takarar da ya fi so gabanin zabukan fidda gwani na 2027, yana mai cewa ba zai tsoma baki a tsarin zaben ’yan takara ba.
Uba Sani ya bayyana haka ne yayin buda baki da ’yan Majalisar Dokokin jihar, inda ya bukaci masu neman mukamai su nemi goyon bayan mambobin jam’iyya maimakon dogaro da uban gida. Ya ce zai mara wa duk wanda ya samu rinjaye a zabukan fidda gwani na APC.
Sai dai ya ce dan takarar da yake goyon baya shi ne Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, a zaben 2027.
Gwamnan ya kuma yi kira ga mambobin jam’iyya su hada kai, yana mai cewa tsaro a Kaduna ya inganta tun bayan hawansa mulki a 2023.



