Gwamnatin Amurka ta kakaba takunkumin biza kan wasu manyan jami’an gwamnatin Rwanda, tana zarginsu da tallafa wa kungiyar ‘yan tawaye ta March 23 Movement M23 da kuma kawo cikas ga zaman lafiya a gabashin jamhuriyar dimukradiyyar Congo.
Jaridar Punch ta rawaito cewa ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta bayyana cewa za ta hana wasu manyan jami’an gwamnatin Rwanda shiga Amurka saboda rawar da ake zargin suna takawa wajen haddasa rikici a yankin.
Sanarwar ta ce ci gaba da tallafa wa M23 da kuma saba yarjejeniyar na kara haddasa tashin hankali tare da kawo barazana ga zaman lafiya a yankin Great Lakes na Afirka.
Amurka ta kuma bukaci bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar su cika alkawurransu, ciki har da gwamnatin Congo ta dakile kungiyar FDLR, yayin da Rwanda kuma za ta janye sojojinta da kayan aikinta na soja daga cikin Congo.



