DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka ta hana wasu jami’an gwamnatin Rwanda shiga ƙasar kan zargin tallafa wa ‘yan tawayen M23

-

Gwamnatin Amurka ta kakaba takunkumin biza kan wasu manyan jami’an gwamnatin Rwanda, tana zarginsu da tallafa wa kungiyar ‘yan tawaye ta March 23 Movement M23 da kuma kawo cikas ga zaman lafiya a gabashin jamhuriyar dimukradiyyar Congo.

Jaridar Punch ta rawaito cewa ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta bayyana cewa za ta hana wasu manyan jami’an gwamnatin Rwanda shiga Amurka saboda rawar da ake zargin suna takawa wajen haddasa rikici a yankin.

Google search engine

Sanarwar ta ce ci gaba da tallafa wa M23 da kuma saba yarjejeniyar na kara haddasa tashin hankali tare da kawo barazana ga zaman lafiya a yankin Great Lakes na Afirka.

Amurka ta kuma bukaci bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar su cika alkawurransu, ciki har da gwamnatin Congo ta dakile kungiyar FDLR, yayin da Rwanda kuma za ta janye sojojinta da kayan aikinta na soja daga cikin Congo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara