Gwamnatin Guinea ta soke rijistar jam’iyyun siyasa 40, ciki har da manyan jam’iyyun adawa guda uku, ta hanyar wata doka da aka fitar da dare.
Matakin ya zo ne kasa da watanni biyu bayan rantsar da shugaban kasar Mamady Doumbouya tsohon shugaban mulkin soja bayan zaben da aka yi a karshen 2025.
Gwamnatin ta ce an rusa jam’iyyun ne saboda sun gaza cika wasu sharudda na doka.



