DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tinubu ta tafka kuskure wajen rabon muƙaman Jakadun Nijeriya – ADC

-

Jam’iyyar ADC mai adawa a Nijeriya ta soki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan sanar da rabon mukaman jakadu zuwa ƙasashen waje, tana mai cewa matakin kuskure ne na diflomasiyya kuma wata alama ce ta rashin kwarewar gwamnati.

A cikin wata sanarwa da Mallam Bolaji Abdullahi, Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, ya fitar, ADC ta ce sanar da mukaman jakadu kafin samun amincewar ƙasashen da za su karɓe su na iya jefa Nijeriya cikin kunyatar diflomasiyya.

Google search engine

Jam’iyyar ta bayyana cewa a ƙarƙashin yarjejeniyar Vienna kan hulɗar diflomasiyya, musamman sashe na 4, dole ne ƙasar da ke aikawa da jakada ta fara neman amincewar ƙasar da za ta karɓe shi kafin sanar da nadin a hukumance.

Ta ce sanar da nadin jakadu sannan a ce ana neman wannan amincewa yana nuna gwamnati ba ta fahimci muhimman ƙa’idojin diflomasiyya ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara