Wani kamfani mai suna Al Itisal Al Jadeed da ke kasar Libiya ne ma’aikatar cikin gidan Nijar ta bai wa kwangilar buga sabon Fesfo ɗin tare da katin shaidar zama ɗan kasa ta kasashen kungiyar AES.
Kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso dai da ke karkashin kungiyar ta AES tun bayan ficewar su daga kungiyar ECOWAS ne suka sanar da samarwa kansu takardar fesfo din kasashen.
Sai dai har kawo yanzu kasar Nijar na amfani da tsohon sanfarin fesfon mai dauke da tambarin kungiyar ECOWAS.



