DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Da izinin Abba aka fitar da kudaden da ake tuhumar mataimakin gwamna – Kwankwasiyya

-

Ƙungiyar Kwankwasiyya a Kano ta musanta zargin almundahana na naira biliyan 1.1 da ake yi wa Mataimakin Gwamna Aminu Abdussalam Gwarzo, inda ta gabatar da takardu da ke nuna an saki kudin ne da izinin Governor Abba Yusuf.

Rahoton ya nuna cewa takardun daga watan Afrilu zuwa Yuni 2024 sun bayyana cewa an tsara rabon kudin N25m ga kowace karamar hukuma domin samar da ruwa da magunguna, wanda ya kai jimillar N1.1bn ga kananan hukumomi 44.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ambato, shugabannin Kwankwasiyya sun ce wannan na nuna cewa Gwarzo ya yi aiki ne bisa doka da izinin gwamna, suna kalubalantar zargin majalisar dokoki a matsayin wani mataki na siyasa.

Majalisar jihar ta ba Gwarzo makonni biyu domin ya mayar da martani kafin a kafa kwamitin bincike kan tuhume-tuhumen da ake a kansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara