Ƙungiyar Kwankwasiyya a Kano ta musanta zargin almundahana na naira biliyan 1.1 da ake yi wa Mataimakin Gwamna Aminu Abdussalam Gwarzo, inda ta gabatar da takardu da ke nuna an saki kudin ne da izinin Governor Abba Yusuf.
Rahoton ya nuna cewa takardun daga watan Afrilu zuwa Yuni 2024 sun bayyana cewa an tsara rabon kudin N25m ga kowace karamar hukuma domin samar da ruwa da magunguna, wanda ya kai jimillar N1.1bn ga kananan hukumomi 44.
Jaridar Daily Trust ta ambato, shugabannin Kwankwasiyya sun ce wannan na nuna cewa Gwarzo ya yi aiki ne bisa doka da izinin gwamna, suna kalubalantar zargin majalisar dokoki a matsayin wani mataki na siyasa.
Majalisar jihar ta ba Gwarzo makonni biyu domin ya mayar da martani kafin a kafa kwamitin bincike kan tuhume-tuhumen da ake a kansa.



