DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kano Abba kabir Yusuf ya gargadi kwamishinoninsa da su gujewa cin amanar gwamnati da kuma fitar da sirrinta

-

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, ya gargadi mambobin majalisar zartarwar jihar da su guji rashin aminci, takaddama a tsakaninsu da kuma fitar da sirrin gwamnati.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin taron majalisar zartarwar karo na 38, inda ya bukaci su hada kai domin ci gaban jihar da walwalar al’umma, yana mai cewa lokacin sabani da zargin juna ya wuce.

Google search engine

Ya kuma jaddada cewa wasu sauye-sauyen siyasa a jihar suka sa shi da wasu manyan shugabanni suka mara wa jam’iyyar APC baya domin samun karin hadin kai da gwamnatin tarayya.

Gwamnan ya kuma tabbatar da murabus din kwamishinoni biyar bayan sauyin siyasar, tare da taya sabbin ‘yan majalisar da suka lashe zaben cike gurbi murna, yana mai bukatar su yi aiki tukuru domin al’ummarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara