DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanatoci 9 sun sauya sheka zuwa jam’iyyar hamayya ta ADC a majalisar dattawan Nijeriya

-

Akalla sanatoci tara daga jam’iyyu daban-daban sun sanar da komawarsu jam’iyyar ADC a zauren majalisar dattawan Nijeriya, lamarin da ya sake sauya fasalin siyasa a majalisar.

Daga cikin sanatocin da suka sauya sheka akwai Aminu Waziri Tambuwal (Sokoto ta Kudu), Enyinnaya Abaribe (Abia ta Kudu), Binos Yaroe (Adamawa ta Kudu), Victor Umeh (Anambra ta Tsakiya), Tony Nwoye (Anambra ta Arewa), Lawal Usman (Kaduna ta Tsakiya), Ogoshi Onawo (Nasarawa ta Kudu), Austin Akobundu (Abia ta Tsakiya) da Ireti Kingibe (FCT).

Google search engine

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta wasikun sauya shekar a zaman majalisar, inda wasu daga cikin sanatocin suka danganta matakin da rikice-rikicen cikin jam’iyyunsu na baya.

Akpabio ya ce sauya shekar na nuna matsalolin cikin gida a jam’iyyun adawa, yana mai cewa har yanzu jam’iyyar APC na da rinjaye a majalisar da sanatoci 87, yayin da ADC ta karu zuwa sanatoci bakwai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara