Majalisar Jami’ar Tarayya ta Dutsin-Ma da ke Jihar Katsina ta amince da dakatar da dalibai 20 bayan a same su da laifin satar jarabawa.
Daraktan yada labarai na jami’ar, Nasiru M. Abdul, ya ce an yanke hukuncin ne a taron majalisar jami’ar karo na 138 bayan duba rahoton kwamitin ladabtar da dalibai.
Mataimakin shugaban jami’ar, Mohammed Khalid Othman, ya ce an dauki matakin ne bisa dokokin jami’ar domin ya zama gargadi ga sauran dalibai da kuma hana karya ka’idojin jarabawa.



