Kungiyar kare hakkin Musulmi, MURIC, ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta tabbatar da samar wa matatun mai na cikin gida isasshen danyen mai domin karfafa samar da makamashi a Nijeriya.
Kungiyar ta yaba wa gwamnati bayan sanarwar dakatar da shigo da man fetur daga waje da NMDPRA ta yi, tana mai cewa matakin ya biyo bayan karuwar samar da fetur a cikin gida.
Daraktan kungiyar, Ishaq Akintola, ya ce ya kamata gwamnati ta ba matatar Dangote cikakken danyen mai domin ta iya aiki yadda ya kamata, yana mai rokon Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya bayar da umarnin hakan domin saukaka farashin mai ga ‘yan Nijeriya.



