Gwamnatin Amurka na shirin tura karin sojoji da jiragen ruwan yaki zuwa yankin Gabas ta Tsakiya yayin da rikici da Iran ke kara tsananta, musamman a yankin.
TRT Afrika ta rawaito cewa ma’aikatar tsaron Amurka na duba yiwuwar tura karin jiragen yaki zuwa yankin domin tallafa wa rundunar da ke can.
Rahoton ya ce sakataren tsaro na Amurka, Pete Hegseth, ya amince da bukatar rundunar ta tura wani bangare na rundunar jiragen ruwa tare da rundunar United States Marine Corps, wadda yawanci ke dauke da jiragen yaki da kusan sojoji 5,000.
Rahoton ya kara da cewa jirgin yaki na ruwa USS Tripoli, wanda ke da sansani a Japan, tare da sojojin da ke cikinsa, sun riga sun nufi yankin Gabas ta Tsakiya domin karfafa rundunar Amurka.



