DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

-

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC.

A cikin wasiƙar da ya aika wa shugaban PDP na mazabar Dogon Daji/Salah Ward a ƙaramar hukumar Tambuwal, mai ɗauke da kwanan wata 15 ga Maris, 2026, Dasuki ya ce rikicin shugabanci da ya daɗe yana addabar jam’iyyar ne ya sa ya yanke shawarar barin jam’iyyar.

Google search engine

Ya bayyana cewa matsalolin cikin gida na jam’iyyar sun raunana ƙarfin PDP wajen taka rawar da ta kamata a matsayin babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya.

Dan majalisar ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tattaunawa da abokan siyasarsa da kuma al’ummar mazabarsa, inda suka nuna damuwa kan halin da jam’iyyar da kuma ƙasar ke ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Ban shirya yin yarjejeniyar sulhu da Iran don kawo karshen yakin da ake yi ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu bai shirya yin wata yarjejeniya da Iran domin kawo karshen rikicin da ke kara tsananta tsakanin kasashen...

Mafi Shahara