DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya ta bai wa dan adawar Guinea-Bissau mafaka

-

Gwamnatin Nijeriya ta amince da bai wa dan adawar Guinea-Bissau Fernando Dias da Costa mafaka, bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar.

 

Google search engine

Wannan mataki dai na kunshe ne cikin wakikar da ministan harkokin wajen Nijeriya Ambasada Yusuf Tuggar ya aike wa da shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS.

 

A cewar gwamnatin Nijeriya, daukar matakin zai taimaka wajen bai wa Fernando Dias tsaro, musamman yadda ya bayyana cewa yana fuskantar barazana tun bayan juyin mulkin.

 

A makon da ya gabata ne dai sojoji suka sanar da karbe iko da mulkin kasar ta Guinea-Bissau, daidai lokacin da ake dakon sakamakon zaben shugaban kasa da ya gudana, lamarin da gwamnatin Nijeriya ta yi Allah-wadai da shi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

Kazalika tsohon shugaban Nijeriya Goodluck Jonathan, wanda ya kasance mai sa ido a zaben kasar ya nuna shakku kan juyin mulkin, yana mai zargin cewa hambararren shugaba Oumarou Sissoco Embalo ne ya kitsa shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara