DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu wata alama da ke nuna cewa Nijeriya za ta rushe – Tukur Buratai

-

Tsohon babban hafsan sojin kasan Nijeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai (rtd), ya ce maganganun da ke cewa Nijeriya na dab da rushewa ba su da tushe.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana hakan a matsayin kalaman da ba su dace ba kuma ba su yi la’akari da tarihin dorewar kasar ba.

Google search engine

Buratai ya ce Nijeriya ta sha tsira daga rikice-rikicen siyasa, matsin tattalin arziki da kalubalen tsaro da ka iya karya wasu kasashe.

A cewarsa, sabon salo na shugabanci mai kishin kasa na fitowa a gwamnati da bangarori daban-daban.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara