DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka ta fara gamsuwa da matakan Tinubu kan tsaron Nijeriya

-

Dan majalisar wakilan Amurka, Riley Moore, ya yaba wa gwamnatin Najeriya kan ceto yara 100 da aka sace daga St. Mary’s Private Catholic School a Papiri, karamar hukumar Agwara, Jihar Neja.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafin X, Moore ya ce wannan ceton yana nuna himma ta gwamnatin Najeriya wajen magance matsalolin tsaro karkashin shugabancin Shugaba Bola Tinubu.

Google search engine

Dan majalisar ya kara da cewa an kafa kwamitin hadin gwiwa tsakanin Amurka da Najeriya don magance zargin tsangwamar Kiristoci a kasar.

Ziyarar Moore ta biyo bayan tattaunawar tsaro tsakanin Mai ba Shugaban Kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, a Washington a watan Nuwamba, inda aka tattauna zargin tsangwamar Kiristoci a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun koka da yawan yada labaran karya a Nijeriya – IGP

Shugaban 'yan sanda a Nijeriya IGP Kayode Egbetokun ya ce babu wata hukuma a Najeriya da ke fuskantar mummunan tasiri daga labaran karya kamar ‘yan...

APC ta dage sauya shekar Gwamnan Taraba zuwa Janairun 2026

Shugaban jam'iyyar APC na Jihar Taraba, Ibrahim Tukur, ya tabbatar cewa gwamnan jihar, Agbu Kefas, zai sauya sheƙa zuwa APC a hukumance a watan Janairu...

Mafi Shahara