DCL Hausa Radio
Kaitsaye

IHR ta bukaci a mayar da rarar kudaden da Alhazan 2025 suka biya

-

Wata kungiyar fararen hula wadda ke gudanar da harkokin da suka shafi addini mai suna ‘Independent Hajj Reporters’ ta sake mika kira ga hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON, da hukumomin jin dadin Alhazai na jihohi su mayar da rarar kudaden da mahajjata sama da dubu 40 suka biya a yayin aikin hajjin 2025.

 

Google search engine

Wata sanarwa da kungiyar ta fitar ta hannun Ibrahim Muhammad, ta ce kowane Alhaji cikin wadanda suka biya kudaden da suka yi yawa, na bin abin da ya kama daga Naira 400,000 zuwa 437,000, dogaro da bambancin da ke tsakanin farashin kasuwar canjin kudade da kuma yadda suka biya a lokacin aikin hajjin na 2025.

 

A cewar kungiyar, kafin wannan lokaci hukumar NAHCON ta bayyana yiwuwar mayar wa da Alhazan kudaden su bayan kammala aikin 2025, tana mai jaddada bukatar yin hakan cikin gaggawa kafin a fara aikin hajjin 2026.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara